BABBAN LABARIN
  RAYUWAR IYALI
Daga UMMANCY UMAR
I-mel: ummancyumar@gmail.com
 
TASKUN DA KANANAN ZAWARAWA SU KE FUSKANTA
BAZAWARA dai ita ce macen da ta tab'a yin aure kuma auren ya mutu. Mutuwar auren nan kuwa ko da wacce irin sanadiyyar ya zo har mijin ta ya sake ta ko kuwa ita da kan ta ne ta nemi sakin. Daga lokacin da ta kammala iddar ta idan Musulma ce ta zama bazawara.

Mace ta kan iya zama bazawara ko da kuwa mijin da ta aura bai sadu da ita ba ajalin auren nasu ya cika, duk da yake da akwai masu ganin cewa muddin dai mace ba ta sadu da mijin ta ba har auren ya mutu ba ta zama bazawara ba, da dai a ce mata ta tab'a yin aure. Ko ma da wacce fassara mutum ya d'auka a d'ayan biyu, bazawara dai ita ce matar da ta tab'a yin aure.

Shi dai aure abu ne wanda a duk lokacin da aka d'aura shi ake fata da kuma burin ganin ma’aurata sun yi zaman mutu-ka-raba ne, amma kuma duk da irin wannan fatar da ma’aurata, ’yan’uwan su abokan arziki da kuma iyaye su ke da shi, idan har ajalin mutuwar zaman aure ya zo tabbas sai an rabu; sai dai kuma idan da rabon ma’auratan su sake dawowa da zama a matsayin miji da mata Allah Ya na iya sake had'awa.

 
Kamar yadda mutuwa ta ke d'aukar duk wanda kwanan sa ya k'are, babu babba babu yaro babu tsoho babu matashi, haka shi kan sa ajali na aure yake, idan ya tashi kawo k'arshen zama babu ruwan sa da shekaru ko mulki ko muk'amin da ma'auratan su ke da shi, kawai shiga yake ya katse igiyar auren.
Kamar yadda idan ajali ya zo ko babu ciwo a mace, haka shi ma ajali na aure yake, wani lokacin ya kan faru ne haka kawai ba tare da wasu ko wani dalili mai k'arfi ba. Wani lokacin kuwa ya na faruwa ne saboda sakacin da mara lafiya ya ke yi wajen k'in kula da bin shawarwarin da likita ya ba shi tun lokacin da aka gano ya na da matsala, to shi ma haka ajalin zaman aure ya ke. Sau tari ma’aurata na k'in bin shawarar da magabatan su su ke ba su ne domin a samu zaman aure mai inganici.

Kamar yadda wani lokacin mara lafiya ya ke d'aukar lokaci ya na jinya, wani lokacin ma har ya kai shi ga kwanciya a asibiti, daga bisani kuma ya mace, haka shi ma zaman aure ya ke. Wani lokacin da zarar an yi aure, to fa zama babu dad'i, yau ana gaban wannan ana sasantawa gobe ana gaban wancan. Wani lokacin ma sai ta kai ga mace ta yi yajin da za ta k'aurace wa gidan mijin nata, daga bisani kuma auren ya mace.

Idan mu ka duba, za mu ga cewa zaman aure da mutuwar aure su na kama da ajali na mutuwa a wani lokaci, amma kuma da akwai inda su ke da bambanci, domin ita mutuwa ba ta da magani kwata-kwata, amma ita mutuwar aure ta na da magani; idan har aka kiyaye wasu abubuwa ana iya samun tsawon rayuwa ta aure, amma idan kuma aka yi masa sakaci irin na mai fama da ciwon hawan jini ko ciwon siga ko kuma sida, nan ta ke mutuwa ta na iya zuwa ta tauke shi.
Duk wani mai fama da ciwon siga, hawan jini ko sida ya na da wuya ki ga cewa ya na wasa da duk wata shawara da likita zai ba shi domin gudun kada mutuwa ta yi awon gaba da shi. Masu irin wannan ciwon kullum su na cikin motsa jiki da kuma gudun cin duk wani abu da likita ya hana su ci tare kuma da shan magani a daidai lokacin da likita ya umurce su. Don haka su ke samun kuzari na tsawon lokaci kafin mutuwa ta zo ta d'auke su.

Wannan duk shimfid'a ce ta yadda sakaci da kuma rashin bai wa ’ya’ya mata mazajen da su ka dace da su da kuma lokacin da ya kamata mu ba da su saboda yanayin zamani ya jawo karin k'ananan zawarawa da auren su ya ke mutuwa a kowace rana ta Allah, kuma har yanzun nan iyaye ba su fuskanci zurfin matsalar da irin wad'annan k'ananan sauta-da-wawa su ke fuskanta ba da kuma bala’in da su ke k'ara kawowa ga al’umma domin su kawo k'arshen wannan abin, don haka kullum abin kamar k'aruwa ya ke yi.

A shekarun baya, idan har miji ya yi sakacin sakin matar sa mai k'arancin shekaru, ko da laifin ta ko ba laifin ta, to tabbas sai ya ga takaici, domin kafin ma ta gaba idda mazaje da dama su na jiran ta. Don haka ne ma ake kiran duk wanda ya saki mace mai k'arancin shekaru wawa, ita kuwa wacce aka sakar ake ce mata sauta-ga-wawa.

A wannan lokacin ya na da matuk'ar wahalar gaske ki ga mace ’yar shekaru 16 zuwa 20 an sake ta, ko da kuwa mijin ta ya na fuskantar matsalar zama da ita. Haka kuma idan har ma an saki mata masu irin wannan shekaru, tabbas sai an samu cewa ta d'an jima a gidan miji ba wai ta yi zama na d'an wasu watanni ne ko shekarun ba a gidan mijin ba.

Irin wad'annan zawarawan a wancan lokacin ana samun su da kamun kai, domin wata daga ranar da auren ta ya mutu har zuwa lokacin yin wani auren nata ba za a gan ta a waje ko a titi ya na yawo unguwa unguwa ba. Wannan ya sa har k'aramar bazawara, har ma da manyan zawarawan wannan zamanin na da bayan an sake su har su yi wani aure ba kowa ya sani ba. Sai dai kawai tsoffin mata da su ke unguwanni ne su ke sani, su ma ganin su ne neman ma wasu mazan zawarawa ne. Don haka duk gidan da aure ya mace a kunnen su, amma ba wai mace
idan auren ta ya mutu a gan ta a titi ta na tallar kan ta ba.

A yau, iyaye sun maida ’ya’yan su haja, duk wanda ya zo ya taya. Idan yana tayawa da maik'o ko an gan shi da alamun mai hannu da shuni ne a ba shi. A yau iyaye burin su shi ne su aurar da ’yar su ga duk wanda ya nuna sha’awar sa ba tare da binciken asalin sa da yanayin iya rik'e masu da kare mutuncin ’yar su ba. A yau iyaye sun k'yale ’ya’yan su su na da k'arfi da ’yancin zab'ar wa kan su mazajen da za su aura ba tare da ba su shawara ko cusa masu tarbiyyar ’ya’yan su, su sukar masu dukkan ragamar rayuwar su ba.

A yau burin iyaye shi ne su dai su aurar da ’yar su ba tare da ba ta tarbiyya ko ilimin addini da na zamani ba. A yau ya na da matuk'ar wahalar gaske ki samu iyayen da za su aurar da ’yar su su zaunar da ita su na mata hud'uba ak'alla na watanni uku kafin zuwan aure domin su karantar da ita yadda rayuwar zaman aure ya ke.

Wad'annan matsalolin da wasu da dama su ne zan kawo muku su idan Allah Ya kai mu fitowa ta gaba domin ganin abin a zahiri yadda iyaye su ke yin sakaci wajen aurar ta ’ya’yan su mata wanda daga bisani kuma bayan namiji ya b'are ta, ya kwad'aita mata sanin dad'in namiji, ya bambanta mata tsakanin ’ya mace da mace, ya sauya mata fasali, ya kwantar mata da nonuwan da aka aurar masa ita da su a tsaitsaye, daga bisani ya ingiza k'yeyar ta, wanda hakan kuma ya sa idan ta dawo gida ta rik'a ganin da ita da uwar ta duk d'aya su ke. Su kuma samari na unguwa da kuma alhazan banza su yi yunk'urin maida ita filin sauke sha’awar su.

Sai dai kuma kafin wannan lokacin, ina son iyaye su yi karatun ta-natsu musamman ga wad'anda ba su riga sun aurar da ’ya’yan su domin ganin cewa masu neman ’ya’yan su da aure ba wad'anda za su sako su ba ne bayan ’yan lokuta na zaman aure. Su kuwa iyayen da aka riga aka sako nasu ’ya’ya, su yi nazarin kuskuren da su ka yi domin kauce wa aukuwar hakan nan gaba.

RAYUWAR IYALI
BABBAN LABARIN
 
 

WASIKU
Ku daina wulakanci
Ai ga irin ta nan!
Mu taya sani addu’a
Abin a yaba ne
Allah ya gafarta ma ta
Allah ya jikan jamila
Allah ya jikan binta
Sakon ta’aziyya da jaje
Ta’aziyya ga sheme
Ki canza rayuwar ki
Allah ya gafarta ma ta
Sako ga shehu kano
Mu ma mun sara mata
’Yan fim ga shawara
Dubi dai jamila haruna
jaje da ta’aziyya
Allah jikan rai
Aikin ku ya yi kyau
Matashiya ga ummancy
‘bolanle’ shirme ne
Ku hada ni da ali nuhu
Rashin ya shafi kowa
Allah ya ba sani lafiya
Sakon ta’aziyya
Fati nijar ta birge ni
Gaisuwa ga ma’aurata
Ku daina la’antar su
Ki na fa da aure!
Rabo mayaudari ne
Allah jikan su
Tahir da binta ina murna
A gaida nakwango
Fantimoti ga gyara
Na ga alfanun fim

LABARAI
An yi taron addu’a ga mamatan marubuta a Kano
’Yan fim na Katsina sun kai wa Rabo caffa
Kotu ta haramta wak'ok'in industiri guda 11
Jami’an Rabo sun fara farautar mawak'a
An Kama Ali Jita Saboda Wak'ar Biki
Mahaifiyar Safiya Musa Ta Kwanta Dama
Ummi Zee-Zee ta zama mawak'iyar Turanci
Zainab da Rabi’u Dalle sun samu Umar
K'ungiyar dillalai na so a raba ta da zalunci
An bugi ’yan fim an hana su kuka
 
   
 
An fara buga mujallar Fim (ISSN 1595-7780) a cikin Maris 1999. Ta na fitowa a kowane wata daga kamfanin INFORMART PUBLISHERS LTD., No. AK 6, Yoruba Road, Kaduna, Nijeriya. Ofishin mu a Kano: Ofishin mujallar Concern, 2nd Floor, Hadiza House, daura da Masallacin Umar Ibn Khattab, Zaria Road, Kano.
A aiko da dukkan wasiku ta adireshin mu na I-mel: mujallarfim@yahoo.com